RMC Hausa
LIVE Radio

MATASHI YA KASHE MATARSHI

Kotun majistre mai lamba 26 ta aike da wani matashi mai suna Adamu Ibrahim gidan gyaran hali bisa zarginsa da hallaka mai dakinsa ta hanyar buga mata dutsen guga a fuska.

Lamarin dai ya faru ne a garin Kwanar Dangora da ke karamar hukumar Kiru ta Jihar Kano.
Tun da fari dai mijin marigayiyar ya ce sabani ne ya shiga tsakaninsa da matarsa dalilin wata mata da ta nuna ba ta son mu’amalarsa da ita.

Sai dai ya ce ya yi ƙoƙarin fahimtar da ita, amma abun ya ci tura, inda ta ce babu ita babu zama da kishiya.

Daga nan ne a cewarsa ta kama shi da kokawa, kuma duk da ihun da yake yi ta ki rabuwa da shi.

Ganin haka ya sanya ya ɗauki dutsen guga akan kujera ya buga mata.
Jaridar Idon gari ta wallafa labarin.

RMC HAUSA TIMES

Post a Comment

Previous Post Next Post