RMC Hausa
LIVE Radio

DOKAR TSAFTA A KADUNA

Gwamnatin Jihar Kaduna ta ayyana Asabar ta ƙarshen kowane wata a matsayin Ranar Tsaftar Muhalli ta Jiha, wani mataki da ta ce za a yi amfani da shi wajen ƙarfafa tsafta, kare lafiyar jama’a da kuma rage barazanar da ke fitowa daga rashin tsafta a faɗin jihar.

A cikin wata sanarwa da Kwamishinan Yaɗa Labarai na jihar, Ahmed Maiyaki, ya fitar, an bayyana cewa aikin tsaftar na farko zai gudana ne a Asabar, 29 ga Nuwamba, 2025, daga ƙarfe 7:00 na safe zuwa 10:00 na safe.

A nasa jawabin, Kwamishinan Muhalli na jihar, Abubakar Buba, ya bayyana wannan shiri a matsayin wani gagarumin mataki na samar da ƙauyuka da birane masu tsafta, aminci da ingantacciyar lafiya. Ya yi kira ga shugabannin al’umma, ƙananan hukumomi, ƙungiyoyin farar hula da sauran masu ruwa da tsaki da su tashi tsaye wajen shajja'a jama’a su fito su ba da tasu gudunmawar.
RMC HAUSA

Post a Comment

Previous Post Next Post