RMC Hausa
LIVE Radio

AN RUSHE SARAKUNA BIYAR NA KANO

Majalisar Dokokin Jihar Kano da ke arewacin Nijeriya ta soke sarakuna biyar da gwamnatin tsohon Gwamna Abdullahi Umar Ganduje ta ƙirƙira.

Majalisar ta ɗauki matakin ne a zaman da ta yi a ranar Alhamis ɗin nan.

A jawabin da ya gabatar, shugaban masu rinjaye na majalisar, Honorabul Lawal Hussaini, ya ce majalisar ta soke dukkan "masarauti biyar da aka ƙirƙira inda za a koma tsarin Masarauta guda ɗaya kamar yadda yake a baya."

Masarautun da aka soke su ne: Birnin Kano, Gaya, Rano, Bichi da Ƙaraye.

A shekarar 2019 dai aka yi wa dokar masarautu a jihar gyara inda aka ƙirƙiro ƙarin masarautu gudu huɗu masu daraja ta ɗaya a jihar.

Post a Comment

Previous Post Next Post