RMC Hausa
LIVE Radio

DANGOTE FOUNDATION

Gidauniya Aliko Dangote Foundation ta jaddada aniyarta na cigaba da ciyar da al’ummar jihar Kano abincin bude baki tunda farkon Ramadan har zuwa karshensa.

Bayanin hakan na zuwa ne a daidai lokacin da ake rabon abincin a wannan rana, ta bakin wakilin gidauniyar ta Dangote na kafafan yada labarai Tukur S Tukur, inda ya bayyana cewa su na iya kokarinsu na ganin sun sauke nauyin da gidauniyar ta dora mu su na tabbatar da adalcin a ya yin rabon abincin.

Tukur S Tukur ya kara da cewa gidauniyar ta Aliko Dangote a bana ta kara kayata abincin da dake bayarwa fiye da na bara, ba ya ga Biredi mai kyau da inganci da ake bayarwa tare da ruwan roba da lemo a kowanne kunshin abincin.

Sannan ya godewa kafafan yada labarai bisa hadin kai da suke bawa kungiyar wajan sanar da duniya ayyukan da suke gudanarwa.

Post a Comment

Previous Post Next Post