Gwamnatin tarayya ta kaddamar da tashar Ruwa ta Tudu acikin Karamar Hukumar Funtuwa ta jihar Katsina.
Sakataren gwamnatin tarayya, Sanata George Akume ne ya wakilci shugaba Tinubu a yayin gudanar da bikin kaddamar da Tashar a ranar Alhamis.
Akume ya ce, gwamnatin tarayya ta kafa tashar Ruwa ta Tudu ne (Dry Inland Port ) a Funtuwa domin bunkasa harkokin kasuwanci da samar da ayyukan yi ga al’ummar jihar Katsina da Nijeriya baki daya.