Majalisar Dattawan Najeriya ta amince da aika sakamakon zaɓe daga rumfunan zaɓe kai-tsaye ta na'ura.
Majalisar ta kuma ce aika sakamakon kai-tsaye ta na'ura zai kasance hanyar farko ta aika sakamakon, amma idan an samu matsalar intanet, INEC za ta yi amfani da takarda a rubuce wajen aika sakamakon kamar yadda aka saba yi a baya.
Sanata Tahir Munguno ne ya gabatar da ƙudirin a lokacin zaman gaggawa da majalisa ta yi kan dokar, yayin da shugaban majalisar ya Godswill Akpabio ya amince da ƙudirin bayan amincewar sauran ƴanmajalisar.
Daga nan ne kuma majalisar ta kafa kwamiti mai mambobi 12 domin yin aiki da majalisar wakilai don tsefe dokokin kamar yadda tsarin amincewa da dokoki ya tanadar.
Category
Siyasa