RMC Hausa
LIVE Radio

KATSINA COLLEGE KATSINA

KATSINA COLLEGE 

Gwamnatin Jihar Katsina tare da tsoffin ɗalibai, sarakunan gargajiya da manyan ‘yan Najeriya sun hallara a Dakin Taro na Kwalejin Dikko domin bikin cika shekaru 100 da kafuwar Kwalejin Dikko, Katsina, inda aka bayyana makarantar a matsayin ginshiƙi mai tarihi wajen gina shugabanci da inganta ilimi a Arewa da Najeriya baki ɗaya.

Da yake jawabi a madadin Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Radda, Mataimakin Gwamna, Malam Faruq Lawal Jobe, ya ce bikin cika shekaru 100 ba taron haɗuwa ba ne kadai, illa murnar tarihin shekaru ɗari na nagarta, hidima da tasiri mai ɗorewa.

Ya bayyana Kwalejin Dikko a matsayin ɗaya daga cikin manyan makarantun sakandare a Najeriya, yana mai cewa tsawon shekaru makarantar ta samar da shugabanni da suka yi fice a fannonin hidimar jama’a, mulki, ilimi, lafiya, injiniya, tsaro, kasuwanci da jagorancin al’umma.

“Duk inda aka ambaci Katsina, ana ganin tasirin Kwalejin Dikko,” in ji Mataimakin Gwamnan, yana jaddada cewa makarantar ba ta tsaya kan takardun shaidar karatu kaɗai ba, sai dai kan tarbiyya, ladabi, kishin ƙasa, jajircewa da hidima.

RMC HAUSA 

Post a Comment

Previous Post Next Post