RMC Hausa
LIVE Radio

SOJOJIN SUN YI RAWAR GANI

Dakarun rundunar haɗin gwiwa ta Joint Task Force North West Operation FANSAN YAMMA sun ƙaddamar da wani gagarumin farmaki kan ƙungiyoyin ’yanta’adda da ’yanbindiga a Jihar Katsina, bayan sacewa da kashe tsohon Manjo Janar Rabe Abubakar.
An fara gudanar da wannan farmaki mai suna Operation CLEAN SWEEP III a ranar 14 ga watan Yuni, inda aka mayar da hankali kan Ƙaramar Hukumar Matazu da maƙwabtanta, wuraren da ƙungiyoyin masu aikata ta’addanci suka daɗe suna addabar al’umma.
A cewar rundunar sojin, an ƙaddamar da aikin ne a matsayin martani ga harin da ya yi sanadin mutuwar tsohon babban jami’in soja, wanda ’yanta’adda da ’yanbindiga suka sace shi tare da matarsa.
Mahukuntan sojin sun bayyana cewa manufar farmakin ita ce gano tare da kawar da waɗanda suka aikata wannan ta’asa, rusa hanyoyin sadarwa da cibiyoyin ayyukan masu laifi a yankin, tare da dawo da zaman lafiya a al’ummomin da abin ya shafa.

Post a Comment

Previous Post Next Post